Gwamnatin Kano tace zata cigaba da wayar da kan Jama’a yadda zasu yi amfani da gidan sauro

Gwamnatin Kano jihar Kano tace ta himmatu wajen cigaba da wayar da akan jama’a game da muhimmancin amfani da gidan sauro.

Kwamishinan lafiya na Jiha Dr Aminu Ibrahim Tsanyawa , ya bayyana hakan a lokacin da yake jawabi a wajen rufe taron gangamin rabon gidajen sauro a fadin Jihar Kano.

Dr. Tsanyawa, yace gangamin rabon gidajen sauron yazo da kalubale iri iri, sai dai bisa taimakon Allah an aiwatar da aikin bisa kokarin gwamnatin Kano da sauran abokan huldarta sun gudanar da aikin rabon gidajen sauron na shekarar 2022 kamar yadda aka tsara.

Manajan shirin rabon gidan sauron a jihar Kano Dr. Abdullahi Isa Kauranmata, kwamishinan ya godewa aniyar Asusun Global Fund, bisa kokarinsa na sanya kudade masu waya wajen inga lafiya da kuma baiwa alummar Jihar Kano kulawar data dace.

Ya kuma yabawa kokarin abokan hulda musamman kungiyoyin da suke cikin shirin, sabo da yadda suka kwashe tsahon kwanaki suna ta kokarin ganin aikin ya tafi dai dai.

Da yake nasa jawabin John Ocholi daga kungiyar kula da lafiyar iyali yace aikin gangamin rabon gidajen sauro a jihar Kano ya samu gagarumar nasara, ya kuma godewa Gwamnan Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje, da Mataimakinsa Dr. Nasiru Yusuf Gawuna, bisa kokarinsu ga alummar Jihar Kano.

Leave a Comment