Yan Nijar Mazauna Kano sun bukaci a dawo da Bazoum kan kujerarsa

Wasu Yan Kasar Niger Mazauna Jihar Kano sun gudanar da Zanga Zangar lumana ta nuna rashin goyon bayan juyin Mulkin da sojoji sukayi a Kasar.

Masu zanga Zangar sunyi kira da a mayar da Muhammad Bazoum Kujerarsa batare da bata lokaci ba.

Sun kuma ja hankalin kungiyar Cigaban Tattalin Arziki kasashen Afrika ta yamma ECOWAS data gudanar da aikinta cikin lumana dan ganin an dawo da Bazoum kujerar Shugabancin Kasar Niger.

Leave a Comment