Shin Matasan Arewa zasu iya kawo sauyi tabangaren Shugabaci a Najeriya?

Daga Abubakar Sale Yakub

Rayuwarku matasa tana da muhammaci ga cigaban Kasa dan suke shiga cikin aikata laifukane?


An ya kuwa Idan aka tafi a haka zaku iya Jan ragamar al’ummar Najeriya kuwa? gaskiya da sake, Idan aka tafi a haka matasa ba zasu taba janragar al’ummar kasarnan ba mutukar baku dai shaye shaye ba.


Ku sani akwai kasashen Duniya da dama da suka jaraba matasa kuma sun sami abin da suke bukata.


Amma haka suka zauna suna aikata laifuka? da shaye shaye? Amsar itace aa,

Domin sunyi karatu kuma iyayensu ba wasu bane duk fa suna kasashen da babu ruwansu da addini basa aikata laifuka.

Dan haka matasan Najeriya zaku iya cin moriyar Damar da aka baku ta shugabantar jama’a matsawar kunyi ilimi kun kuma kaucewa shaye shayen miyagun kwayoyi wanda shine yake lalata rayuwar matasanmu musamman nan Yankin Arewa kususan Jihar Kano.


Shawara Gareku itace kada kuyarda da hudubar Manya ‘yan siyasa na cewar zaku karesu sabi da bukatar Kansu, Rahotanni na nuni da cewa baragurbin ‘Yan siyasa sun tanadi kayan fada sabo daku to kada kukuskura kubi su, Idan gaskiya ne suka hadaku da ‘Ya yansu.

Da wannan nake cewar gyara kayanka bai taba zama sauke muraba ba Muhadu a rubuta na gaba.

Leave a Comment